Skip to content
Mattiyu 27:57-61

Mattiyu 27:57-61

57
Da yamma ta yi, sai ga wani mutum mai arziki daga Arimateya, sunansa Yusuf, wanda shi da kansa almajirin Yesu ne.
58
Ya je wurin Bilatus, ya roƙe shi yă ba shi jikin Yesu. Sai Bilatus ya umarta a ba shi.
59
Yusuf ya ɗauki jikin ya nannaɗe shi da zanen lilin mai tsabta.
60
Sa’an nan ya sa shi a sabon kabarinsa, wanda ya haƙa a dutse. Bayan ya gungura wani babban dutse ya rufe bakin kabarin, sai ya tafi abinsa.
61
Maryamu Magdalin da ɗayan Maryamun, suna zaune a wurin, ɗaura da kabarin.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options