Mattiyu 27:12-14
12
Da manyan firistoci da dattawa suka zarge shi, bai ba da amsa ba.
13
Sai Bilatus ya tambaye shi ya ce, “Ba ka jin shaidar da suke kawowa a kanka?”
14
Amma Yesu bai ce uffam game da ko ɗaya daga cikin zargin da suka yi masa ba. Har gwamna ya yi mamaki ƙwarai.