Skip to content
Mattiyu 26:7-13

Mattiyu 26:7-13

7
wata mace ta zo wurinsa da wani ɗan tulun alabasta na turaren mai tsada sosai, wanda ta zuba a kansa a lokacin da yake cin abinci.
8
Sa’ad da almajiransa suka ga wannan, sai suka yi fushi. Suka ce, “Wannan almubazzaranci fa!
9
Wannan turare ai, da an sayar da shi da kuɗi mai yawa a ba matalauta kuɗin.”
10
Sane da wannan, Yesu ya ce musu, “Me ya sa kuke damun macen nan? Ta yi mini abu mai kyau ne.
11
Matalauta za su kasance tare da ku kullum, amma ni ba zan kasance tare da ku kullum ba.
12
Sa’ad da ta zuba turaren nan a jikina, ta shirya ni ne don jana’izata.
13
Gaskiya nake gaya muku, duk inda aka yi wa’azin bisharan nan a duniya duka, abin da matan nan ta yi, za a riƙa faɗarsa don tunawa da ita.”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options