Mattiyu 26:6-9
6
Yayinda Yesu yake a Betani, a gidan wani mutumin da ake kira Siman Kuturu,
7
wata mace ta zo wurinsa da wani ɗan tulun alabasta na turaren mai tsada sosai, wanda ta zuba a kansa a lokacin da yake cin abinci.
8
Sa’ad da almajiransa suka ga wannan, sai suka yi fushi. Suka ce, “Wannan almubazzaranci fa!
9
Wannan turare ai, da an sayar da shi da kuɗi mai yawa a ba matalauta kuɗin.”
Settings