Skip to content
Mattiyu 22:15-18

Mattiyu 22:15-18

15
Sai Farisiyawa suka yi waje, suka ƙulla yadda za su yi masa tarko cikin maganarsa.
16
Suka aiki almajiransu tare da mutanen Hiridus wurinsa. Suka ce, “Malam, mun san kai mutum ne mai mutunci, kuma kana koyar da maganar Allah bisa gaskiya. Mutane ba sa ɗaukan hankalinka, domin ba ka kula ko su wane ne ba.
17
To, ka gaya mana, a ra’ayinka? Ya dace a biya Kaisar haraji ko a’a?”
18
Amma Yesu da yake ya san mugun nufinsu, sai ya ce, “Ku munafukai, don me kuke ƙoƙarin sa mini tarko?
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options