Skip to content
Mattiyu 17:14-20

Mattiyu 17:14-20

14
Da suka isa wajen taron, sai wani mutum ya zo ya durƙusa a gabansa.
15
Ya ce, “Ubangiji, ka yi wa ɗana jinƙai. Yana da farfaɗiya yana kuma shan wahala ƙwarai. Ya sha fāɗuwa cikin wuta ko ruwa.
16
Na kuma kawo shi wurin almajiranka, amma ba su iya warkar da shi ba.”
17
Yesu ya amsa ya ce, “Ya ku zamani marasa bangaskiya da kuma masu taurinkai, har yaushe zan kasance tare da ku? Har yaushe kuma zan yi haƙuri da ku? Kawo mini yaron a nan.”
18
Yesu ya tsawata wa aljanin, ya kuwa rabu da yaron, nan take yaron ya warke.
19
Sa’an nan almajiran suka zo wurin Yesu a ɓoye suka tambaye shi suka ce, “Me ya sa ba mu iya fitar da aljanin ba?”
20
Ya amsa ya ce, “Saboda kuna da ƙarancin bangaskiya sosai. Gaskiya nake gaya muku, in kuna da bangaskiyar da take ƙanƙanuwa kamar ƙwayar mustad, za ku iya ce wa wannan dutse, ‘Matsa daga nan zuwa can,’ zai kuwa matsa. Babu abin da zai gagare ku.”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options