Mattiyu 12:15-21
15
Da ya gane wannan, sai Yesu ya janye daga wurin. Da yawa suka bi shi, ya kuwa warkar da dukan masu ciwonsu,
16
yana jan musu kunne kada su faɗa wa kowa akan ko shi wane ne.
17
Wannan kuwa domin a cika abin da aka faɗa ta bakin annabi Ishaya ne cewa,
18
“Ga bawana da na zaɓa, ƙaunataccena, wanda nake farin ciki da shi; zan sa Ruhuna a kansa, zai kuma yi shelar adalci ga al’ummai.
19
Ba zai yi faɗa ko yă ɗaga murya ba, ba kuwa wanda zai ji muryarsa a kan tituna.
20
Kyauron da ya tanƙwasa ba zai karye shi ba. Fitilar da ta yi kusan mutuwa ba zai kashe ta ba, sai ya jagoranci adalci zuwa ga nasara.
21
Cikin sunansa al’ummai za su dogara.”
Settings