Skip to content
Markus 16:9-13

Markus 16:9-13

9
Da Yesu ya tashi daga matattu da safe, a ranar farko ta mako, ya fara bayyana ga Maryamu Magdalin, wadda ya fitar da aljanu bakwai daga cikinta.
10
Ta je ta gaya wa waɗanda dā suke tare da shi, waɗanda kuma suke makoki da kuka.
11
Da suka ji cewa Yesu yana da rai, har ma ta gan shi, ba su gaskata ba.
12
Daga baya Yesu ya bayyana a wani kamanni dabam ga biyunsu, yayinda suke tafiya ƙauye.
13
Waɗannan kuwa suka koma suka shaida wa sauran, amma su ma ba su gaskata ba.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options