Markus 16:9-11
9
Da Yesu ya tashi daga matattu da safe, a ranar farko ta mako, ya fara bayyana ga Maryamu Magdalin, wadda ya fitar da aljanu bakwai daga cikinta.
10
Ta je ta gaya wa waɗanda dā suke tare da shi, waɗanda kuma suke makoki da kuka.
11
Da suka ji cewa Yesu yana da rai, har ma ta gan shi, ba su gaskata ba.
Settings