Skip to content
Markus 13:28-37

Markus 13:28-37

28
“To, sai ku yi koyi da itacen ɓaure. Da zarar rassansa suka yi taushi, ganyayensa kuma suka toho, kun san cewa damina ta yi kusa ke nan.
29
Haka ma, in kuka ga waɗannan abubuwa suna faruwa, ku san cewa ya yi kusan zuwa, yana ma dab da bakin ƙofa.
30
Gaskiya nake gaya muku, zamanin nan ba zai shuɗe ba sai duk abubuwan nan sun faru.
31
Sama da ƙasa za su shuɗe, amma kalmomina ba za su taɓa shuɗewa ba.
32
“Game da wannan rana ko sa’a kuwa, ba wanda ya sani, ko mala’ikun da suke sama, ko Ɗan, sai Uban kaɗai.
33
Ku lura fa! Ku zauna a shirye! Don ba ku san lokacin da shi zai zo ba.
34
Yana kama da mutumin da zai yi tafiya. Yakan bar gidansa a hannun bayinsa, kowa da nasa aikin da aka sa shi, yă kuma ce wa wanda yake gadin ƙofa, yă yi tsaro.
35
“Saboda haka, sai ku zauna a shirye, domin ba ku san lokacin da maigidan zai dawo ba, ko da yamma ne, ko da tsakar dare ne, ko lokacin da zakara na cara ne, ko kuma da safe ne.
36
In ya zo kwaram, kada ka bari yă tarar da kai kana barci.
37
Abin da na faɗa muku, na faɗa wa kowa. ‘Ku yi tsaro!’ ”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options