Skip to content
Markus 11:15-19

Markus 11:15-19

15
Da suka kai Urushalima, sai Yesu ya shiga filin haikalin, ya fara korar waɗanda suke saya da sayarwa a can. Ya tutture tebur na masu musayar kuɗi, da kujerun masu sayar da tattabaru,
16
ya kuma hana kowa yă ratsa da a filin haikali ɗauke da kayan ciniki.
17
Da yake koya musu, sai ya ce, “Ashe, ba a rubuce yake ba cewa, ‘Za a kira gidana, gidan addu’a na dukan al’ummai ba’?Amma ga shi kun mai da shi ‘kogon ’yan fashi.’”
18
Manyan firistoci da malaman dokoki suka ji wannan, sai suka fara neman hanyar da za su kashe shi, gama suna jin tsoronsa, saboda dukan taron suna mamakin koyarwarsa.
19
Da yamma ta yi, sai Yesu da almajiransa suka bar garin.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options