Skip to content
Markus 10:41-45

Markus 10:41-45

41
Da sauran goman suka ji wannan, sai suka yi fushi da Yaƙub da Yohanna.
42
Yesu ya kira su ya ce musu, “Kun sani waɗanda aka san su da mulkin al’ummai sukan nuna musu iko, hakimansu ma sukan gasa musu iko.
43
Ba haka ya kamata yă zama da ku ba. A maimakon, duk wanda yake so yă zama babba a cikinku, dole yă zama bawanku.
44
Duk wanda kuma yake so yă zama na farko, dole yă zama bawan kowa.
45
Gama ko Ɗan Mutum ma, bai zo domin a bauta masa ba, amma don yă yi bauta, yă kuma ba da ransa fansa saboda mutane da yawa.”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options