Markus 10:10-12
10
Da suna cikin gida kuma, sai almajiran suka tambayi Yesu game da wannan.
11
Ya amsa ya ce, “Duk wanda ya saki matarsa, ya auri wata, yana da laifin aikata zina a kan matar da ya saki.
12
In kuma ta saki mijinta ta auri wani, ta yi zina ke nan.”