Luka 9:53-56
53
Amma mutanen ƙauyen ba su karɓe shi ba, don yana kan hanyar zuwa Urushalima ne.
54
Da almajiransa, Yaƙub da Yohanna suka ga haka, sai suka yi tambaya suka ce, “Ubangiji, kana so mu kira wuta ta sauka daga sama ta hallaka su?”
55
Amma Yesu ya juya, ya kwaɓe su.
56
Sai shi da almajiransa suka tafi wani ƙauye.
Settings