Skip to content
Luka 8:51-56

Luka 8:51-56

51
Da ya iso gidan Yayirus, sai ya hana kowa yă bi shi cikin ɗakin, sai dai Bitrus, da Yohanna, da Yaƙub, da kuma mahaifin da mahaifiyar.
52
Ana cikin haka, dukan mutanen kuma sai kuka da makoki suke ta yi, domin yarinyar. Sai Yesu ya ce, “Ka daina yin kuka, ba tă mutu ba, tana barci ne.”
53
Sai suka yi masa dariya, da yake sun san cewa, ta mutu.
54
Amma Yesu ya kama ta a hannu ya ce, “Diyata, tashi.”
55
Ruhunta ya dawo, kuma ta tashi, nan take. Yesu ya ce musu, su ba ta wani abu tă ci.
56
Iyayenta suka yi mamaki, amma ya ba su umarni kada su faɗa wa kowa abin da ya faru.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options