Skip to content
Luka 9:1-6

Luka 9:1-6

1
Bayan da Yesu ya tara Sha Biyun wuri ɗaya, sai ya ba su iko da izini na fitar da dukan aljanu, da na warkar da cututtuka.
2
Ya kuma aike su, su yi wa’azin mulkin Allah, su kuma warkar da marasa lafiya.
3
Ya ce musu, “Kada ku ɗauki kome don tafiyar, wato, ba sanda, ba jaka, ba burodi, ba kuɗi, ba riga na biyu.
4
Duk gidan da kuka sauka, ku zauna nan sai kun bar garin.
5
In mutane ba su karɓe ku ba, sa’ad da kun bar garinsu, ku karkaɗe ƙurar ƙafafunku don shaida a kansu.”
6
Sai suka tashi suka shiga ƙauye zuwa ƙauye suna wa’azin bishara, suna warkar da marasa lafiya a ko’ina.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options