Luka 24:39-45
39
Ku duba hannuwana da ƙafafuna. Ai, ni ne da kaina! Ku taɓa ni ku ji, ai, fatalwa ba ta da nama da ƙashi, yadda kuke gani nake da su.”
40
Da ya faɗi haka, sai ya nuna musu hannuwansa da ƙafafunsa.
41
Kuma har yanzu, suna cikin rashin gaskatawa, saboda murna da mamaki, sai ya tambaye su, “Kuna da abinci a nan?”
42
Suka ba shi ɗan gasasshen kifi,
43
ya karɓa ya ci a gabansu.
44
Ya ce musu, “Wannan shi ne abin da na gaya muku tun ina tare da ku cewa, dole a cika kome da aka rubuta game da ni, a cikin Dokar Musa, da Annabawa, da kuma Zabura.”
45
Sai ya wayar da tunaninsu don su fahimci Nassi.
Settings