Luka 24:39-43
39
Ku duba hannuwana da ƙafafuna. Ai, ni ne da kaina! Ku taɓa ni ku ji, ai, fatalwa ba ta da nama da ƙashi, yadda kuke gani nake da su.”
40
Da ya faɗi haka, sai ya nuna musu hannuwansa da ƙafafunsa.
41
Kuma har yanzu, suna cikin rashin gaskatawa, saboda murna da mamaki, sai ya tambaye su, “Kuna da abinci a nan?”
42
Suka ba shi ɗan gasasshen kifi,
43
ya karɓa ya ci a gabansu.
Settings