Luka 24:36-39
36
Suna cikin wannan zance, sai ga Yesu da kansa tsaye a tsakiyarsu. Sai ya ce musu, “Salama a gare ku!”
37
Suka firgita, suka tsorota, suna tsammani fatalwa ce suka gani.
38
Sai ya ce musu, “Don me kuke damuwa, kuke kuma shakka a zuciyarku?
39
Ku duba hannuwana da ƙafafuna. Ai, ni ne da kaina! Ku taɓa ni ku ji, ai, fatalwa ba ta da nama da ƙashi, yadda kuke gani nake da su.”
Settings