Luka 2:41-45
41
Kowace shekara, iyayen Yesu sukan je Urushalima don Bikin Ƙetarewa.
42
Da Yesu ya cika shekaru goma sha biyu, sai suka tafi Bikin bisa ga al’ada.
43
Bayan Bikin, da iyayen suka kama hanya don su koma gida, sai Yesu, yaron nan, ya tsaya a Urushalima, ba da saninsu ba.
44
Su kuwa sun ɗauka yana tare da su, saboda haka, suka yi ta tafiya har na yini guda. Sa’an nan suka fara nemansa cikin ’yan’uwansu da abokansu.
45
Da ba su gan shi ba, sai suka koma Urushalima nemansa.
Settings