Tsallake zuwa abun ciki
Firistoci 8:31-36

Umarnin Keɓewar Kwana Bakwai

Firistoci 8:31-36
31
Sai Musa ya ce wa Haruna da ’ya’yansa maza, “Ku dafa naman a ƙofar Tentin Sujada, ku kuma ci shi a can tare da burodi daga kwandon naɗi, yadda na umarta, cewa, ‘Haruna da ’ya’yansa maza za su ci shi.’
32
Sa’an nan ku ƙone sauran naman da kuma burodin.
33
Kada ku bar ƙofar Tentin Sujada har kwana bakwai, sai ranakun naɗi suka cika, gama naɗinku zai ɗauki kwana bakwai.
34
Abin da aka yi a yau umarni ne daga Ubangiji don yin kafara saboda ku.
35
Dole ku kasance a ƙofar Tentin Sujada dare da rana har kwana bakwai, ku kuma yi abin da Ubangiji yake bukata, don kada ku mutu; gama abin da aka umarce ni ke nan.”
36
Saboda haka Haruna da ’ya’yansa maza suka yi kome da Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options