Tsallake zuwa abun ciki
Firistoci 8:1-5

Shiri don Keɓewa

Firistoci 8:1-5
1
Ubangiji ya ce wa Musa,
2
“Kawo Haruna da ’ya’yansa maza, ka ɗauki rigunansu, man keɓewa, bijimi domin hadaya don zunubi, ’yan raguna biyu da kuma kwandon da yake da burodi marar yisti,
3
ka kuma tara dukan jama’a a ƙofar Tentin Sujada.”
4
Sai Musa ya yi yadda Ubangiji ya umarce shi, jama’a kuwa suka taru a ƙofar Tentin Sujada.
5
Sai Musa ya ce wa jama’ar, “Ga abin da Ubangiji ya umarta a yi.”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options