Makoki 3:1-6
1
Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.
2
Ya kore ni, ya sa na yi tafiya a cikin duhu maimakon a cikin haske;
3
ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.
4
Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.
5
Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni da baƙin ciki da kuma wahala.
6
Ya sa na zauna a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu da jimawa.
Settings