Mahukunta 12:13-15
13
Bayansa, Abdon ɗan Hillel, daga Firaton, ya shugabanci Isra’ila.
14
Yana da ’ya’ya maza arba’in da ’yan taɓa kunne talatin, waɗanda suka hau jakuna saba’in. Ya shugabanci Isra’ila shekara takwas.
15
Sa’an nan Abdon ɗan Hillel ya mutu, aka kuwa binne shi a Firaton a Efraim, a ƙasar tudu ta Amalekawa.
Settings