Skip to content
Mahukunta 11:4-11

Mahukunta 11:4-11

4
Ana nan, sa’ad da Ammonawa suka kai wa Isra’ilawa hari,
5
dattawan Gileyad suka je suka nemo Yefta daga ƙasar Tob.
6
Suka ce masa, “Ka zo ka zama mana shugaba, don mu yaƙi Ammonawa.”
7
Yefta ya ce musu, “Ba kun ƙi ni kuka kuma kore ni daga gidan mahaifina ba? Me ya sa kuke zuwa wurina yanzu sa’ad da kuke cikin wahala?”
8
Mutanen Gileyad suka ce masa, “Duk da haka, muna juyo wajenka yanzu, ka zo tare da mu mu yaƙi Ammonawa, za ka kuma zama shugaban duk wanda yake zama a Gileyad.”
9
Yefta ya ce, “A ce kun dawo da ni in yaƙi Ammonawa, Ubangiji kuwa ya ba da su a hannuna, zan zama shugabanku?”
10
Dattawan Gileyad suka ce, “Ubangiji ne shaidanmu; za mu yi duk abin da ka ce.”
11
Saboda haka Yefta ya tafi tare da dattawan Gileyad, mutanen kuwa suka naɗa shi shugabansu da kuma sarkinsu. Ya kuwa maimaita dukan maganarsa a gaban Ubangiji a Mizfa.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options