Skip to content
Yoshuwa 13:15-23

Yoshuwa 13:15-23

15
Ga abin da Musa ya ba kabilar Ruben bisa ga iyalansu.
16
Abin da ya kama daga Arower a gefen kwarin Arnon, da kuma daga garin da yake tsakiyar kwarin, da dukan ƙasar tudu kusa da Medeba
17
zuwa Heshbon, da dukan garuruwan kan tudu, haɗe da Dibon, Bamot Ba’al, Bet-Ba’al-Meyon,
18
Yahza, Kedemot, Mefa’at,
19
Kiriyatayim, Sibma, Zeret Shahar kan tudu cikin kwari,
20
Bet-Feyor, gangaren Fisga da Bet-Yeshimot,
21
dukan garuruwan da suke kan tudu da dukan masarautar Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulki a Heshbon. Musa ya yi nasara da shi, da shugabannin Midiyawa, wato, Ewi, Rekem, Zur, Hur, da Reba, sarakunan Sihon, waɗanda suka zauna a ƙasar.
22
Ƙari a kan waɗanda aka kashe a yaƙi, Isra’ilawa suka kashe Bala’am ɗan Beyor da takobi don yana duba.
23
Gefen Urdun shi ne iyakar mutanen Ruben. Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne gādon mutanen Ruben, bisa ga iyalansu.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options