Skip to content
Yohanna 8:31-36

Yohanna 8:31-36

31
Sai Yesu ya ce wa Yahudawan da suka gaskata da shi, “In dai kun riƙe koyarwata, ku almajiraina ne da gaske.
32
Sa’an nan za ku san gaskiya, gaskiyar kuwa za tă ’yantar da ku.”
33
Sai suka amsa masa suka ce, “Ai, mu zuriyar Ibrahim ne kuma ba mu taɓa bauta wa kowa ba. Yaya za ka ce za a ’yantar da mu?”
34
Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, duk mai yin zunubi bawan zunubi ne.
35
Bawa dai ba shi da wurin zama na ɗinɗinɗin a cikin iyali, amma ɗa na gida ne har abada.
36
Saboda haka in Ɗan ya ’yantar da ku, za ku ’yantu da gaske.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options