Yohanna 8:31-33
31
Sai Yesu ya ce wa Yahudawan da suka gaskata da shi, “In dai kun riƙe koyarwata, ku almajiraina ne da gaske.
32
Sa’an nan za ku san gaskiya, gaskiyar kuwa za tă ’yantar da ku.”
33
Sai suka amsa masa suka ce, “Ai, mu zuriyar Ibrahim ne kuma ba mu taɓa bauta wa kowa ba. Yaya za ka ce za a ’yantar da mu?”
Settings