Skip to content
Yohanna 17:6-9

Yohanna 17:6-9

6
“Na bayyana ka ga waɗanda ka ba ni a duniya. Su naka ne; kai ka ba ni su sun kuma yi biyayya da maganarka.
7
Yanzu sun san cewa duk abin da ka ba ni daga gare ka ya fito.
8
Na ba su kalmomin da ka ba ni sun kuwa karɓa. Sun san tabbatacce daga wurinka na fito. Sun kuma gaskata kai ka aiko ni.
9
Ina addu’a dominsu. Ba domin duniya nake addu’a ba, amma domin waɗanda ka ba ni, gama su naka ne.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options