Skip to content
Yohanna 16:1-4

Yohanna 16:1-4

1
“Na faɗa muku wannan duka, domin kada ku bauɗe.
2
Za su kore ku daga majami’a; lalle, lokaci yana zuwa da duk wanda ya kashe ku, zai ɗauka yana yin wa Allah hidima ne.
3
Za su yi waɗannan abubuwa ne domin ba su san Uba ko ni ba.
4
Na faɗa muku wannan, domin in lokacin ya yi, ku tuna na gargaɗe ku. Ban faɗa muku wannan tun da fari ba domin ina tare da ku.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options