Yohanna 16:1-4
1
“Na faɗa muku wannan duka, domin kada ku bauɗe.
2
Za su kore ku daga majami’a; lalle, lokaci yana zuwa da duk wanda ya kashe ku, zai ɗauka yana yin wa Allah hidima ne.
3
Za su yi waɗannan abubuwa ne domin ba su san Uba ko ni ba.
4
Na faɗa muku wannan, domin in lokacin ya yi, ku tuna na gargaɗe ku. Ban faɗa muku wannan tun da fari ba domin ina tare da ku.
Settings