Yohanna 12:20-22
20
To, akwai waɗansu Hellenawa a cikin waɗanda suka haura don su yi sujada a Bikin.
21
Suka zo wurin Filibus, wanda yake daga Betsaida ta Galili, da roƙo. Suka ce, “Ranka yă daɗe, muna so mu ga Yesu.”
22
Sai Filibus ya je ya gaya wa Andarawus, Andarawus da kuma Filibus suka gaya wa Yesu.