Skip to content
Ayuba 8:1-7

Ayuba 8:1-7

1
Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
2
“Har yaushe za ka gama faɗa waɗannan abubuwa? Maganganunka ba su da amfani.
3
Allah ba mai shari’ar gaskiya ba ne? Ko Maɗaukaki yakan yi abin da ba daidai ba?
4
Lokacin da ’ya’yansa suka yi masa zunubi, yakan bar su su sha wahalar da zunubi yake kawowa.
5
Amma in za ka dubi Allah ka roƙi Maɗaukaki,
6
in kai mai tsarki ne, kuma mai adalci, ko yanzu ma zai taimake ka, yă mayar maka iyalinka da farin cikinka.
7
Ko da yake za ka fara da kaɗan, duk da haka za ka gama da samu mai yawa.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options