Ayuba 7:16-21
16
Ba na so in zauna da rai; ba zan rayu ba har abada. Ku rabu da ni; rayuwata ba ta da amfani.
17
“Mene ne mutum har da ka kula da shi haka, har ka mai da hankali a kansa,
18
har kake duba shi kowace safiya, kake kuma gwada shi koyaushe?
19
Ba za ka ɗan daina kallo na ba ko ka rabu da ni na ɗan lokaci?
20
In na yi zunubi, me na yi maka, kai mai lura da mutane? Don me ka sa ni a gaba? Na zame maka kaya mai nauyi ne?
21
Me ya sa ba za ka gafarta mini laifofina ba? Gama na kusa kwantawa cikin ƙasa; za ka neme ni, amma ba za ka same ni ba.”
Settings