Ana nuna aya 1 tare da mahallin da ke kewaye.
1
“Ka yi kira in kana so, amma wa zai amsa maka? Wurin waɗanne tsarkaka za ka juya?
2
Fushi yana kashe wawa, ƙyashi kuma yana kashe marar azanci.
3
Ni ma na ga wawa yana cin gaba, amma nan da nan gidansa ya zama la’ananne.
4
’Ya’yansa suna cikin hatsari, ba wanda zai tsaya musu a gaban alƙali,