Gudun tsuntsayen farauta na ɗabi’a
26
“Ko ta wurin hikimarka ce shirwa take firiya take kuma baza fikafikanta zuwa kudu?
27
Ko da umarninka ne shaho yake firiya ya kuma yi sheƙarsa a can sama?
28
Yana zama a kan dutse yă zauna a wurin da dare; cikin duwatsu ne wurin zamansa.
29
Daga can yake neman abincinsa; idanunsa suna gani daga nesa.
30
’Ya’yansa suna shan jini, inda akwai waɗanda aka kashe nan za a same shi.”
Settings