Zum Inhalt springen
Ayuba 38:4-18

Ayuba 38:4-18

4
“Kana ina lokacin da na aza harsashen duniya? Gaya mini, in ka sani.
5
Wane ne ya zāna girmanta? Ba shakka ka sani! Wane ne ya ja layin aunawa a kanta?
6
A kan me aka kafa tushenta, ko kuma wa ya sa dutsen kan kusurwarta,
7
yayinda taurarin safe suke waƙa tare dukan mala’iku kuma suka yi sowa don farin ciki.
8
“Wane ne ya rufe teku a bayan ƙofofi, lokacin da ya burtsatso daga cikin ciki.
9
Lokacin da na yi wa gizagizai riga na kuma naɗe su a cikin duhu sosai,
10
sa’ad da na yi masa iyaka na sa masa ƙofofi da wurin kullewa.
11
Sa’ad da na ce ga iyakar inda za ka kai, ga inda raƙuman ruwanka za su tsaya?
12
“Ko ka taɓa ba safiya umarni ko kuma ka sa asuba ta fito,
13
don ta kama gefen duniya ta kakkaɓe mugaye daga cikinta?
14
Ƙasa ta sāke siffa kamar laka da aka yi wa hatimi; ta fito a fili kamar riga.
15
An hana mugaye haskensu, hannun da suka ɗaga an karya shi.
16
“Ko ka taɓa tafiya zuwa maɓulɓulan teku, ko kuma ka taɓa zuwa cikin zurfin lungun teku?
17
Ko an taɓa nuna maka ƙofar mutuwa? Ko ka taɓa ganin ƙofar inuwar duhun mutuwa?
18
Ko ka gane fāɗin duniya? Gaya mini, in ka san wannan duka.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options