Skip to content
Ayuba 38:1-11

Ayuba 38:1-11

1
Sa’an nan Ubangiji ya amsa wa Ayuba. Ya ce,
2
“Wane ne wannan da yake ɓata mini shawarata da surutan wofi?
3
Ka sha ɗamara kamar namiji; zan yi maka tambaya, za ka kuwa amsa mini.
4
“Kana ina lokacin da na aza harsashen duniya? Gaya mini, in ka sani.
5
Wane ne ya zāna girmanta? Ba shakka ka sani! Wane ne ya ja layin aunawa a kanta?
6
A kan me aka kafa tushenta, ko kuma wa ya sa dutsen kan kusurwarta,
7
yayinda taurarin safe suke waƙa tare dukan mala’iku kuma suka yi sowa don farin ciki.
8
“Wane ne ya rufe teku a bayan ƙofofi, lokacin da ya burtsatso daga cikin ciki.
9
Lokacin da na yi wa gizagizai riga na kuma naɗe su a cikin duhu sosai,
10
sa’ad da na yi masa iyaka na sa masa ƙofofi da wurin kullewa.
11
Sa’ad da na ce ga iyakar inda za ka kai, ga inda raƙuman ruwanka za su tsaya?
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options