12
“Ko ka taɓa ba safiya umarni ko kuma ka sa asuba ta fito,
13
don ta kama gefen duniya ta kakkaɓe mugaye daga cikinta?
14
Ƙasa ta sāke siffa kamar laka da aka yi wa hatimi; ta fito a fili kamar riga.
15
An hana mugaye haskensu, hannun da suka ɗaga an karya shi.