Ayuba 33:1-7
1
“Amma yanzu, Ayuba, ka saurari abin da zan ce; ka sa hankali ga kowane abin da zan faɗa.
2
Zan yi magana; kalmomina suna dab da fitowa daga bakina.
3
Abin da zan faɗa gaskiya ne daga cikin zuciyata; bakina zai faɗi gaskiyar abin da na sani.
4
Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.
5
Ka amsa mini in za ka iya; ka yi shirin fuskanta ta.
6
Ni kamar ka nake a gaban Allah; ni ma daga ƙasa aka yi ni.
7
Kada ka ji tsorona, ba abin da zai fi ƙarfinka.
Settings