Skip to content
Ayuba 32:15-22

Ayuba 32:15-22

15
“Mamaki ya kama su kuma ba su da abin cewa; kalmomi sun kāsa musu.
16
Dole ne in jira yanzu da suka yi shiru, yanzu da suke tsaye a wurin ba su da amsa.
17
Ni ma zan faɗi nawa; ni ma zan faɗi abin da na sani.
18
Gama ina cike da magana, kuma ruhun da yake cikina yana iza ni;
19
a ciki ina kamar ruwan inabi wanda aka rufe a cikin kwalaba, kamar sabuwar salkar ruwan inabi mai shirin fashewa.
20
Dole in yi magana in sami lafiya; dole in buɗe baki in ba da amsa.
21
Ba zan nuna wa wani sonkai ba, ko kuma in yi wa wani daɗin baki ba;
22
gama da a ce na iya daɗin baki, da wanda ya yi ni ya ɗauke ni daga nan tuntuni.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options