Skip to content
Ayuba 30:26-30

Ayuba 30:26-30

26
Duk da haka sa’ad da nake begen abu mai kyau, mugun abu ne ya zo; Sa’ad da nake neman haske, sai duhu ya zo.
27
Zuciyata ba tă daina ƙuna ba; ina fuskantar kwanakin wahala.
28
Na yi baƙi ƙirin, amma ba rana ce ta ƙona ni ba. Na tsaya a cikin mutane, na kuma yi kuka don taimako.
29
Na zama ɗan’uwan diloli, na zama abokan mujiyoyi.
30
Fatar jikina ta yi baƙi tana ɓarewa; jikina yana ƙuna da zazzaɓi.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options