Skip to content
Ayuba 3:1-11

Ayuba 3:1-11

1
Bayan wannan Ayuba ya buɗe baki ya la’anta ranar da aka haife shi.
2
Ayuba ya ce,
3
“A hallaka ranar da aka haife ni, da kuma daren da aka ce, ‘An haifi jariri namiji!’
4
Bari ranan nan ta zama duhu; kada Allah yă kula da ita; kada rana tă yi haske a wannan rana.
5
Bari duhu da inuwa mai duhu ta sāke rufe ta; gizagizai kuma su rufe ta; duhu kuma ya rufe haskenta.
6
Bari duhu mai yawa yă rufe daren nan; kada a haɗa ta cikin kwanakin shekara, ko kuma cikin kwanakin watanni.
7
Bari daren yă zama marar amfani; kada a ji wata sowa ta farin ciki.
8
Bari waɗanda suke la’anta ranaku su la’anta wannan rana su waɗanda suke umartar dodon ruwa.
9
Bari taurarinta na safe su zama duhu; bari ranar tă yi ta jiran ganin haske amma kada tă gani,
10
gama ba tă hana uwata ɗaukar cikina, don ta hana ni shan wahalan nan ba.
11
“Me ya sa ban mutu ba da za a haife ni, ko kuma in mutu sa’ad da ana haihuwata ba?
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options