Ayuba 29:12-16
12
domin na ceci matalauta waɗanda suka nemi taimako, da marasa mahaifi waɗanda ba su da wanda zai taimake su.
13
Mutumin da yake bakin mutuwa ya sa mini albarka. Na faranta wa gwauruwa zuciya.
14
Na yafa adalci ya zama suturata; gaskiya ita ce rigata da rawanina.
15
Ni ne idon makafi kuma ƙafa ga guragu.
16
Ni mahaifi ne ga masu bukata; na tsaya wa baƙo.
Settings