Ayuba 23:13-17
13
“Amma ya tsaya shi kaɗai, kuma wa ya isa yă ja da shi? Yana yin abin da yake so.
14
Yana yi mini abin da ya shirya yă yi mini, kuma yana da sauran irinsu a ajiye.
15
Shi ya sa na tsorata a gabansa; sa’ad da na yi tunanin wannan duka, nakan ji tsoronsa.
16
Allah ya sa zuciyata ta yi sanyi; Maɗaukaki ya tsorata ni.
17
Duk da haka duhun bai sa in yi shiru ba, duhun da ya rufe mini fuska.
Settings