Ayuba 17:1-5
1
Na karaya, kwanakina sun kusa ƙarewa, kabari yana jirana.
2
Ba shakka masu yi mini ba’a suna kewaye da ni; idanuna suna ganin tsokanar da suke yi mini.
3
“Ya Allah, ka ba ni abin da ka yi mini alkawari. Wane ne zai kāre ni?
4
Ka rufe zuciyarsu yadda ba za su iya ganewa ba, saboda haka ba za ka bari su yi nasara ba.
5
In mutum ya juya wa abokansa baya don a ba shi wata lada ’ya’yansa za su makance.
Settings