Tsallake zuwa abun ciki
Irmiya 33:23-26

Allah ya sake tabbatar da yarjejeniya da Isra’ila

Irmiya 33:23-26
23
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
24
“Ba ka lura ba cewa waɗannan mutane suna cewa, ‘Ubangiji ya ƙi masarautai biyu da ya zaɓa’? Saboda haka suka rena mutanena ba sa ƙara ɗaukansu a matsayin al’umma.
25
Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘In ban kafa alkawarina game da rana da kuma game da dare ba in kuma gyara dokokin sama da duniya ba,
26
to zan ƙi zuriyar Yaƙub da na Dawuda bawana ba zan kuma zaɓi ɗaya daga cikin ’ya’yansa maza ya yi mulki a kan zuriyar Ibrahim, Ishaku da Yaƙub ba. Gama zan mayar da wadatarsu in kuma yi musu jinƙai.’ ”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options