Skip to content
Hosiya 8:1-4

Hosiya 8:1-4

1
“Ka sa kakaki a leɓunanka! Gaggafa tana a bisan gidan Ubangiji domin mutane sun tā da alkawarina suka kuma tayar wa dokata.
2
Isra’ila ta yi mini kuka, ‘Ya Allahnmu, mun yarda da kai!’
3
Amma Isra’ila sun ƙi abin da yake mai kyau; abokin gāba zai fafare su.
4
Suna naɗa sarakuna, ba da izinina ba; sun zaɓa shugabanni ba da yardanta ba. Da azurfa da zinariya sun ƙera gumaka wa kansu wanda zai kai zuwa ga hallakarsu.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options