Skip to content
Farawa 8:15-19

Farawa 8:15-19

15
Sa’an nan Allah ya ce wa Nuhu,
16
“Fito daga jirgin, kai da matarka da ’ya’yanka maza da matansu.
17
Ka fitar da kowane iri halitta mai rai da take tare da kai waje, tsuntsaye, dabbobi, da dukan halittu masu rarrafe a ƙasa, don su yi ta haihuwa, su yi yawa, su ƙaru a duniya.”
18
Sai Nuhu ya fito tare da matarsa da ’ya’yansa maza da matan ’ya’yansa,
19
da kowace irin dabba, da kowane mai rarrafe, da kowane irin tsuntsu, da kowane irin abu da yake tafiya a bisa duniya, suka fito daga jirgi daki-daki bisa ga irinsu.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options