Tsallake zuwa abun ciki
Farawa 25:1-6

Zuriyar Ibrahim ta baya

Farawa 25:1-6
1
Ibrahim ya auro wata mace, mai suna Ketura.
2
Ta haifa masa Zimran, Yokshan, Medan, Midiyan, Ishbak da Shuwa.
3
Yokshan shi ne mahaifin Sheba da Dedan. Zuriyar Dedan su ne mutanen Ashur, da mutanen Letush, da kuma mutanen Lewummin.
4
’Ya’yan Midiyan maza su ne, Efa, Efer, Hanok, Abida, da kuma Elda’a. Dukan waɗannan zuriyar Ketura ce.
5
Ibrahim ya bar wa Ishaku kome da ya mallaka.
6
Amma yayinda Ibrahim yake da rai, ya ba wa ’ya’yan ƙwarƙwaransa maza kyautai, ya kuma sallame su daga ɗansa Ishaku zuwa ƙasashen gabas.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options