Skip to content
Ezra 10:15-17

Ezra 10:15-17

15
Yonatan ɗan Asahel, da Yazehiya ɗan Tikba su ne kaɗai ba su yarda da wannan shirin ba, sai Meshullam da Shabbetai Balawe kuma suka goyi bayansu.
16
Sai waɗanda suka dawo daga bauta suka yi yadda aka zartar. Ezra firist ya zaɓi mutane waɗanda su ne shugabannin iyalai, ɗaya daga kowane sashe, aka rubuta sunan kowannensu. A ranar ɗaya ga watan goma kuwa suka zauna don su yi binciken waɗannan abubuwa.
17
A rana ta farko ga watan farko, suka gama da bincike duk waɗanda suka auri baƙin mata.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options